Similar Songs
Credits
PERFORMING ARTISTS
Ado Gwanja
Performer
COMPOSITION & LYRICS
Ado Gwanja
Songwriter
PRODUCTION & ENGINEERING
Isa Gombe
Producer
Lyrics
Ahayye matan Arewa kun mai mata
Allah tsare idanuwan ku ranar kallo
Eh mana
Eh ahayye matan Arewa kun mai mata
Allah tsare idanuwan ku ranar kallo
In dai har inda rato sarkin hattara
Domin mai banbara ba bai yin tauna
Ko an tinzira ba'a fin gaban hakura mun sani
Dan hannu bayi kare hasken rana
Su kara, kuda kar su kara suna gani
Gwanja yau nazamo gutunbun bauna
Bana kallon makiyi asara
Domin sai da irinsu za'a kai jan kololuwa
Mata kuji Gwanja be da dake
Ku taso muci duniya da tsinke
Mubar masu nawa suje su noke
Ni dai nai damarar gudu da falke (toh)
Idan nayi da kyau ku bani maki
Ni mata na Arewa zan wa take
Da karba, karba akanyi danga
Idan kai daya kayi to da sake
Ni da mata tafiyar mu naga ta dau haske
Inda duk sun kayi za'a bi su bana yin makowa
Ga zarena na dinka taguwa ta
Duk dai nasan duniya dai da fadi
Zamani yayi wa baka gata
Bishi kar kai masa hassada da kaudi
Lamarin Allah kuga wanda yaja
To da rami a gaban sa zaya fadi
Mai salo in kaji yayi karka tanka
Nayi mata suka ce abin da dadi
Mai kare kama karen ka tunda kura tazo
Bani hanu baka kan na koshi in hau neman ruwa
Ke kaza daina tone-tone karki tono mana abin duniya
Da rana, da rana tsaka
Ko a taro ba duniya idan har an zo
Bayi kaiwa sai yan Arewa mata sun zo
Ashe dai kaska tana da haushin kifi
Shi ko girman dan saniya yakai yayai tozo
Shi ko girma Allah ka baiwa kowa yaso
Masanin darajar mata an kacewa gwarzo
Ashe dai mu damunar tazo
Muyi dua'i dan kar mu dinga kukan ansha ruwa
Da haushi in guje a dawo mini
Da dadi in iya a kawo mini
Zane dai an kayin sa tun ran gini
Ban adawa, tunda rabbana yayai hani
Toh akwai nau, babu wanda zai sam mini
Tinda baiwa gashi rabbana yayai mini
Bani fatan mu tsaya mu dinga kallon kallo
Haka Allah ya nufe ni tunda dai har nai tsintuwa
Ban da mata wa zamu bawa girma
Tunda na kula hakkin su nada dama
In zumunci suka so ka baka fama
In na bar su fadan wanda zana kama
Wasu zunde karshen su yin nadama
Tunda kifi ya fahimci masu koma
Tunda mata na Arewa basu gulma
Dole in nuna ajinsu nada girma
Ko ka boye, koma ka bayyana kai ka jiyo
Banda Allah wazaya gane hausar yar tsutsuwa
Writer(s): Bello Hassan, Ado Isah Gwanja
Lyrics powered by www.musixmatch.com